
BBC News Hausa
@bbchausa • 2,549,964 subscribers
BBC Hausa - Fiye da shekara 60 na labaran duniya da rahotannin da suka shafi rayuwarku
Shorts
Videos

Ƴan gudun hijira daga Sudan da ke jihar Kano sun roƙi hukumomi su sa hannu wajen inganta rayuwarsu ta hanyar samar musu da gidaje da ilimi. Sun gudu daga Sudan ne saboda yaƙin da ya ɓarke, lamarin da ya kai ga ƙasar ke fuskantar barazanar wargajewa. Tace hoto - Fatima Othman
BBC News Hausa21,934 просмотров • 6 дней назад

Ministan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa (mai ritaya) ya faɗi manyan abubuwan da suka sa aka kasa shawo kan matsalar tsaro a ƙasar da kuma salon da zai yi amfani da domin kawo ƙarshen matsalar. Ya kuma bayyana aniyarsa ta gina katanga a wasu iyakokin Najeriya.
BBC News Hausa315,931 просмотров • 6 месяцев назад

Cutar farfadiya, lalura ce da take shafar ƙwaƙwalwa ta yadda take wargaza wani saiti mai kama da wayoyin lantarki. Zainab Ammuna Abubakar, wadda ta assasa gidauniyar Ikiru Epilepsy Foundation ta bayyana yadda ake kula da masu wannan lalura. 🎥 - Abba Auwalu
BBC News Hausa119,493 просмотров • 3 месяцев назад

Mahmoud Sadis Buba (Abin Alʼajabi) wani ɗan takarar majalisar tarayya mai wakiltar Sabon Garin Zariya ne da ke jan hankali saboda yanayin halittarsa. Abin Alʼajabi ya shaida wa BBC dalilin da ya sa ya fito wannan takara. 🎥 - Isa Umar Ladu/Abba Auwalu Furodusa - Aminu Kutama
BBC News Hausa75,284 просмотров • 2 месяцев назад

Iyalan matar nan, Ummulkhairi da aka ƙone a Kaduna sun zargi baturen ƴan sandan yankin da miƙa ta ga mutanen da suka kashe ta. Mijin matar, Aliyu Muhammad da sauran ƴan uwanta sun ce an yi mata hakan ne sakamakon zarginta da satar yara. Tace hoto - Fatima Othman
BBC News Hausa34,747 просмотров • 1 месяц назад

Mai magana da yawun shugaban Najeriya, Daneil Bwala ya ce babu wani abin da ya shiga tsakaninsa da ɗan takarar shugaban ƙasa na ADC, Atiku Abubakar, wanda suka yi aiki tare a zaɓen 2023, sai dai sharrin masu son haɗa faɗa. 🎥 - Abba Auwalu Furodusa - Aminu Kutama
BBC News Hausa29,737 просмотров • 26 дней назад

Kwanaki kaɗan bayan da aka gudanar da zanga-zanga a faɗin Najeriya saboda tsadar rayuwa, mataimakin shugaban ƙasar, Sanata Kashim Shettima ya ce gwamnatin tarayya na sane da yanayin da ake ciki kuma ta soma ɗaukar matakan magance matsalolin da ake fama da su.
BBC News Hausa447,994 просмотров • 1 год назад