
TRT Afrika Hausa
@trtafrikaHA • 47,198 subscribers
Afirka, tsantsarta
Shorts
Videos

Matashiyar nan 'yar Jihar Gomba a arewa maso gabashin Nijeriya, Maryam Ibrahim Dan Azumi wacce ta lashe Musabaƙar Karatun Alƙur'ani ta Duniya ɓangaren mata da aka gudanar a Saudiyya inda ta wakilci Nijeriya, ta bayyana sirrin nasararta a wajen musabaƙar. Maryam, wacce a yanzu haka take aji huɗu a jami'a ta kuma bayyana wa TRT Afrika Hausa irin horon da suke samu a gida wajen haddar Alƙu'ani. Shekaru biyu da suka wuce yayarta Hajara Ibrahim Dan Azumi ta lashe Musabaƙar Alƙur'ani a ƙasar Jordan inda ta wakilci Nijeriya.
TRT Afrika Hausa213,450 views • 23 days ago

Shugaban Nijar Janar Abdourahamane Tiani ya ce sun jima da bai wa gwamnatin Nijeriya bayanan sirri game da yadda Faransa take shirin kafa sansanin 'yan ta'adda na ƙungiyar Lakurawa a Nijeriya. Ya bayyana haka ne a wata hira da gidan talabijin na Nijar a ranar Laraba inda ya yi zargin cewa gwamnatin Nijeriya na da masaniya game da ayyukan Lakurawa da kuma yin watsi da shawarwarin da suka ba ta game da ‘yan ta’addan.
TRT Afrika Hausa892,113 views • 1 year ago
No more content to load

